1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Turkiyya zai gana da Shugaban Hamas

April 20, 2024

Shugaban Turkiyya na ganawa da shugaban kungiyar Hamas ta Falasdinawa domin tattauna halin rikici da Zirin Gaza ke ciki.

https://p.dw.com/p/4f0VY
Shugaban Turkiyya da shugabannin Falasdinawa da kuma Hamas
Hoto: Mustafa Kamaci/Anadolu Agency via REUTERS

Shugaba Racep Tayyip Erdogan na Turkiyya ne ganawa da shugaban kungiyar Hamas ta Falasdinu, Ismail Haniyeh a birnin Santanbul domin tattauna halin rikicin da Zirin Gaza ke ciki.

Sai dai ba a bayyana karin bayani kan yanayin da tattaunawar za ta kasance ciki ba tsakanin bangarorin biyu. A ranar Larabar da ta gabata ce dai, Haniyeh ya gana da ministan harkokin wajen Turkiyya, Hakan Fidan a Qatar kan batun tsagaita bude wuta a Zirin da kuma sakin wadanda aka tsare da su.

A farkon wannan makon ne dai Shugaba Erdogan dai ya soki Firanministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a kan abun da ya bayyana a matsayin kisan kiyashi a Gaza. Sai dai kuma Isra'ila ta nisanta kanta da kalaman shugaban.

Ko da yake duk da zafafan kalaman na Shugaba Erdogan, a baya-bayan nan Turkiyar ta yi kokarinta na shiga tsakani domin sasanta rikicin na Gaza.