1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Corona na barazana ga ilimi a duniya

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 29, 2021

Firaministan Birtaniya Boris Johnson da shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta na daukar nauyin wani taro na hadin gwiwa kan harkokin ilimi a duniya.

https://p.dw.com/p/3yGex
Mali Symbolbild Bildung
Tashe-tashen hankula ma na illa ga bangaren ilimi, musamman na yara a yankin SahelHoto: picture-alliance/AP Photo/UNICEF/Dicko

Shugabannin biyu wato Firaministan Birtaniya Boris Johnson da Shugaba Uhuru Kenyatta na Kenyan dai, sun bukaci shugabannin kasa da kasa su taimaka wajen farfado da harkokin ilimi a kasashen da ke fama da tashe-tashen hankula. Taron dai zai fi mayar da hankali kan kasashen yankin Sahel da ke zaman yankin da ke fama da tarin matsaloli musammana na tsaro. A shekarar da ta gabata kadai, makarantu 5,000 aka rufe sakamakon fargabar tsaro da tashe-tashen hankula da kuma sace mutane domin neman kudin fansa, musamman a Tarayyar Najeriya.

A wata hira da ta yi da tashar DW, tsohuwar firaministar Ostraliya Julia Gillard da a yanzu ke shugabantar shirin hadin gwiwa na bunkasa ilimi na duniya, ta nunar da cewa akwai gagarumar faragaba kan yadda corona ka iya mayar da harkokin ilimi baya a duniya baki daya. Koda ya ke Gillard ta ce sun dauki darasi yayin annobar Ebola, ta yadda a yanzu suke kokarin tabbatar da ganin kowanne yaro ya koma makaranta, sai dai ta ce akwai sauran aki a gaba.