1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harkokin ilimi a Najeriya da Nijar

Lateefa Mustapha Ja'afar
September 16, 2021

A kasashe masu tasowa da dama, ana fuskantar kalubale kala-kala a fannin ilimi. Haka lamarin yake a kasashen Tarayyar Najeriya da makwabciyarta Jamhuriyar Nijar.

https://p.dw.com/p/40PaO
Nigeria Jangebe 300 Schulmädchen von bewaffneten Männern entführt
Makarantun Najeriya na fuskantar barazanar tsaroHoto: Sunday Alamba/AP/picture alliance

Sau da dama, ana fuskantar kalubale a fannin ilimi musamman a kasashe masu tasowa. A Jamhuriyar Nijar da Tarayyar Najeriya, matsalolin tsaro na taimakawa wajen samun koma baya a fannin ilimi musamman na makarantun firamare da sakandare. A baya-bayan nan dai, ana ta kwashe daliban makarantun firamare da sakandare har ma da jami'o'i a jihohin yankin Arewa maso Yammacin Najeriya.

A baya ma dai an samu irin wannan matsalar a yankin Arewa maso Gabashin kasar daga 'yan ta'adxdan Boko Haram, sai dai lamarin ya fi kamari a yanzu haka a yankin Arewa maso Yamman da 'yan bindiga suka taso gaba. Ana dai alakanta wadannan matsaloli da yawan faduwar jarrabawa da ake samu daga dalibai, musamman jarrabawar kammala sakandare da ta shiga jami'a.

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna

Rahotanni da Sharhuna