Goyan baya ga Mohamadou Issoufou
February 10, 2011Talla
Bayan da jam'iyyar Africa Lumana, wadda ta zo ta uku a zaɓen shugaban ƙasa zagaye na farko ta bayyana goyan bayanta ga jam'iyyar PNDS Tarayya ta ɗan takarar neman shugaban ƙasa Mouhammadou Isoufou, a halin yanzu haka ana daɗa samun ƙarin jam'iyyun siyasa dake nuna goyan bayansu a fafutukar neman a dama da su a sabuwar gwamnatin da za a naɗa a Janhuriyar Nijer nan gaba a wannan shekara. Ga dai wasu rahotannin da wakilanmu na biranen Tahoua da Agades suka turo mana akan ire-iren martanin da jam'iyyun siyasar ke mayarwa a sassa daban-daban na ƙasar.
Mawallafi: Ahmad Tijani Lawal
Edita: Mohammad Nasiru Awal